Posts

Showing posts from May, 2024

Zuwa shekara mai zuwa muna fatan Gwamnan Kano Zai Bude Makarantun Da Muka Gyara Prof Dahiru Sale Muhammed

Image
Shugaban Hukumar kula da makarantun Kimiyya da Fasaha na jihar Kano Asso. Prof Dahiru Sale Muhammed ya bayyana cewa nan bada jimawa ba Gwamnatin jiha Kano Zata bude wasu makarantu da suka gyara a zuwan su cikin shekara daya. Babban Sakataren ya bayyana hakan ne a ranar Talatar nan yayin da yake zantawa da wasu Gidajen Jaridu a wata ziyara da suka kaimasa. Prof Dahiru yace a wannan lokaci sun dukufa wajen ganin sun farfado da Ilimin kimiyya da Fasaha a fadin Jihar Kano baki daya dan kara Bunkasa harkokin koyo da koyarwa. Dr Dahiru Sale, yace sun shirya tsaf wajen ganin sun shirya bita ta musamman ga Malaman su, wanda yace duk karshen Zango su cigaba da bada wannan bita. Gwamna Abba Kabir ya bullo da Ayukan Cigaba a fadin Jihar Kano-Hauwa Isah Sojoji Sun Kama Wani Malami Da Matarsa A Abuja “Kasancewar zamani na canzawa yake kowane lokaci yasa zamu cigaba da bada damar ba Malaman bita, wanda nan gaba zamu gayyaci manyan malaman Duniya dan su bada bita a wannan jiha tamu.. Sai dai Dr Dahir

Ba Zan iya kamanta yadda naji lokacin da Gwamna yabani shugabancin KSSMB :Dr. Kabir Zakirai

Image
Babban sakataren hukumar kula da Hukumar malaman sakandire na jihar Kano Dr. Kabir Ado Zakirai ya bayyana kudurin gwamnatin jihar Kano karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf na kokarin dawo da martabar ilimi a jihar. Dr. Kabir Ado ya bayyana hakane a wata zantawa da manema labarai lokacin da suka kai masa ziyarar aiki ranar Talatar nan. Zakirai yace idan za’a iya tunawa cewa gwamna ya bayyana kudurin sa na dawo da martabar ilimi a fadin jihar Kano tun lokacin da ake yakin neman zaben da ya gabata. Babban Sakataren ya bayyana irin koma baya da ya samu lokacin da ya samu kansa a matsayin shugaban wannan hukuma ta kula da sakandire da malamanta na jiha Kano. Zuwa shekara mai zuwa muna fatan Gwamnan Kano Zai Bude Makarantun Da Muka Gyara Prof Dahiru Sale Muhammed Sojoji Sun Kama Wani Malami Da Matarsa A Abuja “Gaskiya mun sani kamar yadda kuka sani a wancan tsohuwar gwamnat an samu rashin kulawa matuka wajen abinda yashafi wannan hukuma,amma zuwa gwamna Abba Kabir ya kawo hanyoyin da ake warwar

QUALIFYING EXAMINATION MASS FAILURE

Image
Gwamnatin Jahar Kano bisa jagorancin His Excellency Eng Abba Kabir Yusuf ta kafa kwamitin yin bincike akan gano dalilan da su ka sa aka samu muguwar faduwa a jarrabawar Qualified Examination ta shekarar 2023.   Comrade Auwal S.Jae @teachersmedia2252024

Qualifying Examination mass failure 2023

Image
  Gwamnatin Jahar Kano bisa jagorancin His Excellency Eng Abba Kabir Yusuf ta kafa kwamitin yin bincike akan gano dalilan da su ka sa aka samu muguwar faduwa a jarrabawar Qualified Examination ta shekarar 2023.   Comrade Auwal S.Jae @teachersmedia2252024

QUALIFYING EXAMINATION FAILURE

Image
EDUCATIONQUALIFYING EXAM: KNSG To Investigate Mass Failure  Kano state Government has established a committee to investigate the mass failure in the recently concluded qualifying examinations for Senior Secondary Schools. A statement signed by the Director Public Enlightenment Ministry of Education Balarabe Abdullahi Kiru shared with THESTENTORNEWS, explained that the committee’s terms of reference include determining the extent of the examination failures, examining the causes of the mass failure, and assessing whether there was compliance with the established procedures for releasing the results. The statement added that the Committee will look into how the private students participate in the examination.  It is also part of the Committee’s responsibility to advise the government on whether to continue with the examination process or otherwise ” said the statement. According to the statement, the committee which has been given one week to submit its report, will be chaired by Alhaj

SAKATAREN ILIMI NA KMC LGEA

Image
Sakataren Ilimi na Karamar Hukumar Birni Comrade Nura Sulaiman ya bayyana cewa yana da kyakkyawan shirin na aiki kafada da kafada da shugabannin sassan na sashen ilimi da shugabannin makarantu na karamar hukumar don ganin an ciyar da ilimi gaba a fadin karamar . Comarade Nura ya a lokacin taron da yayi da shugabannin makaranatar firamare ta a kwalli mai taken SABUWAR MUNICIPAL akan harkar ilimi inda ya shaidawa Al’umma cewar dole ne kowa ya tsaya tsayin daka akan aikinsa don kai wa ga nasara. Sakataren ilimi ya yi kira ga shugabanin makarantu da kungiyoyin Al,umma gatan makaranta da kungiyoyin tsofaffin Dalibai da kungiyar malamai da iyayen yara da kungiyar iyaye mata, da suzo a hadu domin ciyar da ilimi gaba musamman ta fannin karfafa zuwan yara makaranta da kuma dawo da yaran da suka daina zuwa makaranta da inganta ilimin yara mata. Comrade Nura ya hori malaman makaranta da su kara jajircewa domin inganta ilimi a karamar hukumar don bawa gwamnati kwarin gwiwa akan kudirinta na habbak

An rantsar da sabbin ANCOPS na kano

Image
*ANCOPS KANO CHAPTER*   A yau ranar Talata 14/5/2024 Maigirma Kwamishinan ilimi na jahar kano Alhaji Umar Haruna Doguwa ya sa babban lauyan Ministry of Education ya rantsar da *sabbin shuwagabannin riƙo na ANCOPS Kano chapter* a Dakin taro na gidan Murtala dake ofishin Commissioner.  Maigirma Kwamishinan ilimin ya ja wa shuganin da aka rantsar kunne akan lallai su tsaya su yi aiki tukuru da kuma gaskiya. Sabanin yadda tsohuwar ANCOPS da aka sauke a dalilin yawan karɓe-karɓe da aka same su dasu , wanda shi ne dalilin sauke su kamar yadda Maigirma Kwamishinan ilimin ya bayyana a yau. Sannan ya ƙara tabbatar wa da jama'ar Kano ce wa, Gwamnatin Kano ta shirya tsaf wajan gyara makarantu da samar da kayan aiki da kuma wadatar da malamai a kowacce makaranta. Haka kuma Kwamishinan ya koka matuƙa akan yawan samun over staff da ake samu a wasu makarantun a inda ya tabbatar da wata makaranta mai Ajujuwa guda goma sha uku, amma kuma tana ɗauke da malamai sama da guda tamanin.  Comrade Auwal S.

BA ZA MU SAKE YADDA DA CIN ZARAFIN MALAMAN MAKARANTA BA

Image
 NUT KANO STATE WING   A yau Litinin 13/5/2024 Maigirma State NUT Chairman *Comrade Baffa Ibrahim Garko* ya kai ziyarar nuna jaje makarantar *GJSS Ɗanmali* akan mummunan harin da wasu iyayen yara su ka kai wa Vice principal ta makarantar a satin da ya gabata .   Maigirma Chairman ya ƙara jaddada wa al'umma jahar Kano musamman iyayen yara da sauran mutanen gari ce wa, daga yanzu ƙungiyar malaman makaranta ta NUT ba za ta sake zuba ido ba wani ko wasu mutane su ke shiga har makaranta su na cin zarafin malaman makaranta ba. Ya kuma ƙara da ce wa, duk wanda aka sake samu da aika irin wannan munanan halaye na cin zarafin malaman makaranta, to sai inda ƙarfinsa ya ƙare.  Comrade Baffa ya ƙara da ce wa, lallai malaman makaranta su tsaya su kare aikinsu yadda ya kamata. Kuma ƙun ƙungiyar NUT kofarta abuɗe ta ke wajan ganin an share wa kowanne malami hawayenshi a duk inda ya ke a duk faɗin jahar Kano.   A inda shi kuma shugaban makarantar GJSS Ɗanmali ya ce , tabbas shi a yanzu ma ya fara s

NUT KANO STATE WING BA ZA MU ƘARA YADDA DA CIN MUTUNCIN MALAMAI BA

Image
 NUT KANO STATE WING   A yau Litinin 13/5/2024 Maigirma State NUT Chairman *Comrade Baffa Ibrahim Garko* ya kai ziyarar nuna jaje makarantar *GJSS Ɗanmali* akan mummunan harin da wasu iyayen yara su ka kai wa Vice principal ta makarantar a satin da ya gabata .   Maigirma Chairman ya ƙara jaddada wa al'umma jahar Kano musamman iyayen yara da sauran mutanen gari ce wa, daga yanzu ƙungiyar malaman makaranta ta NUT ba za ta sake zuba ido ba wani ko wasu mutane su ke shiga har makaranta su na cin zarafin malaman makaranta ba. Ya kuma ƙara da ce wa, duk wanda aka sake samu da aika irin wannan munanan halaye na cin zarafin malaman makaranta, to sai inda ƙarfinsa ya ƙare.  Comrade Baffa ya ƙara da ce wa, lallai malaman makaranta su tsaya su kare aikinsu yadda ya kamata. Kuma ƙun ƙungiyar NUT kofarta abuɗe ta ke wajan ganin an share wa kowanne malami hawayenshi a duk inda ya ke a duk faɗin jahar Kano.   A inda shi kuma shugaban makarantar GJSS Ɗanmali ya ce , tabbas shi a yanzu ma ya fara s

KANO STATE OF EMERGENCY ON EDUCATION

Image
*KANO STATE EMERGENCY ON EDUCATION*  A Alhamis 2/5/2024 ƙungiyoyin Fara hula dana ma'aikatun ilimi su ka gabatar da buƙatarsu ga Gwamnatin Kano ta hannun Honourable Commissioner of Education Alhaji Umar Haruna Doguwa na neman Gwamnatin Jahar Kano da ta zartar da dokar taɓaci akan harkar ilimi (state of Emergency on Education ). Saboda matsanancin taɓarɓarewar ilimi da aka samu a jahar Kano.   Ƙungiyoyin da suka gabatar da wannan koke sun haɗa da:- - NUT Kano - ANCOPS - AOPSHON - SBMC - PTA da sauransu. - AKY KWANKWASIYYA EDUCATION SUPPORT  Comrade Auwalu S. Ja'e @teachersmedia20240504

NLC KANO TA YI WATSI DA BATUN KARIN ALBASHI

Image
Kungiyar kwadago ta kasa NlC reshen jihar kano tayi watsi da batun Karin mafi karancin albashi da kashi 35 Cikin dari da gwamnatin tarayya ta yiwa ma;aikatan kasar nan Da yake zantawa da wakilinmu rabiu ahmad kofar mazugal ta wayar tarho, shugaban kungiyar kungiyar na jihar kano kwamarade kabiru inuwa ya bayyana cewa kafin amincewa da duk wani Karin mafi karancin albashi akwai wasu matakai da ya kamata gwamnatin tabi Kwamarade kabiru yace daga cikin matakan akwai samar da kwamitin hadin guiwa tsakanin gwamnatin tarayya da kuma kungiyoyin kwadago da kuma mikawa majalisar tarayya batun domin ya zama doka Dan haka acewar kwamarade kabiru inuwa, wannan Karin da gwamnatin tarayya tayi basu gamsu dashi ba, kasancewar batabi ka;idar yadda yakamata tayi ba

KANO MAY DAY 2024 CELEBRATION

Image
Kungiyar kwadago ta jahar Kano tare da kafatanin ƙungiyoyin da su ke ƙarƙashinta su ka gabatar da taronta na murnar zagayowar ranar ma'aikata ta Duniya (Workers Day 2024) a inda ƙungiyar malaman makaranta (NUT) ta zama zakaran gwaji a faretin gaisuwa ga maigirma mataimakin Gwamna. Wanda hakan ne ya sa aka bawa ƙungiyar NUT Babban Kofi na karramawa. Saboda kwazo da su ka nuna a wajan yin faretin girmamawa da kuma gudanar da  aikin koyarwa ba tare da nuna banbanci ba wajan haɗa kan malaman makaranta da kuma bawa gwamnati shawarwari na gari.  Comrade Baffa Ibrahim Garko shugaban ƙungiyar NUT reshen jahar Kano ya nuna farin cikinsa akan wannan karramawa da aka yi wa NUT ta jahar Kano. . NLC  ta jahar Kano ta nuna ce wa, NUT ce kadai ƙungiyar malaman makaranta ta hakika  wadda take ƙarƙashinta. A inda Secretary NLC ya ce , Ƙungiyar ASUSS ba ta cikin jeran ƙungiyoyin da su ke ƙarƙashin Tutar NLC ta ƙasa . Amma an gode musu tunda sun zo taron da bai shafe su ba.