Mun gaji da yin funcen albashi- Auwal S

Ma'aikatan jahar Kano sun koka akan yawan funce da ake musu akan albashinsu na wata-wata ba bisa ka'ida ba.
  Wasu daga Ma'aikatan jahar Kano sun yi Allah wadai da yawan zaftare musu albashi da ake yi a duk wata daga cikin albashinsu ba tare da ka'ida ba. Kamar yadda wasu ma'aikata su ka sanar da manema labarai a ranar Asabar 1/3/2025 , a inda su ke ce wa, kamata yai ma a yi musu ƙari saboda halin matsi da ake ciki ba ake yi musu funce ba.
  Wasu ma'aikatan da ba su yadda a fadi sunayensu ba , sun ce an yanke musu sama da Naira 33,000 wasu kuma Naira 22,000 a inda wasu kuma aka yankar musu Naira 18,000.
  Mun nemi masu ruwa da tsaƙi akan wannan lamari amma abun ya ci tura.

Comments

Popular posts from this blog

NUT KANO BA TA SAN WANI ALWAILARI MEDIA PRESS BA- Comrade Auwal Shuaibu

PROFESSOR RAKAKA YA RASU

NUT DALA TA KAI WA IYALAN M. AISHA TALLAFI- COMRADE AUWAL S