Gwamnati za ta kafe sunayen ma'aikata da albashinsu dan kowa ya san abun da za a biya shi domin gujewar matsalar da aka fuskanta a baya- Auwal S. TMCS Media Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar wa ma’aikatan gwamnati a jihar cewa za a biya su albashinsu kafin bukukuwan Eid-el-Fitr, (idin Karamar sallah) wanda ake sa ran zai fara daga ranar 25 ga Maris. Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG), Faruk Ibrahim, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Litinin. Wakilin mu na Kwankwasiyya Reporters, Comr Muhammad M Alasan, ya rawaito mana cewa an shirya taron manema labarai ne domin sanar da al’umma matakan da gwamnatin jiha ke dauka don gujewa matsalolin da aka fuskanta wajen biyan albashin watan Fabrairu. Yayin da yake jawabi a taron, Alhaji. Umar Faruk Ibrahim ya bayyana cewa gwamnati na sane da bukukuwan Sallah karama, da ke karatowa, kuma za ta tabbatar da biyan albashin watan Maris kafin bikin. A cewarsa, ma’aikatan gwamnati a jihar za su tabbatar da sahihanci...
Comments
Post a Comment