A yau ranar Juma'a 19/4/2024 ƙungiyar TUC reshen jahar Kano ta rantsar da sabbin shugabanninta a inda aka rantsar da Comrade Hajiya Maryam Yahaya Musa a matsayin Chairperson kamar yadda doka ta tanada.
Hukumar kula da makarantun primary schools ta fara bawa dukkanin ma'aikatanta damar fara futar da payment slip na albashi daga watan Junairu na shekarar 2024 daga yanzu. A inda hukumar bisa haɗin guiwa da kungiyar malaman makaranta reshen jahar Kano (NUT) su ka sanar. Comrade Baffa Ibrahim Garko shugaban kungiyar NUT shi ne ya ci alwashin ganin an zamanantar da wannan tsari na albashi kamar yadda ake yi a sauran ma'aikatu na Duniya baki daya. Comrade Baffa ya ƙara isar da sakon godiya ga Maigirma Gwamnan jahar Kano His Excellency Eng Abba Kabir Yusuf tare da shugaban hukumar ilimin baidaya bisa yadda da amincewa da wannan tsari. Comr. Auwalu S. Jae dauke da rahoto teachersmedia@3/3/2024
Kungiyar Malaman Makaranta reshen jahar Kano ta magantu akan rashin sawa wasu malaman makaranta kudin promotion wadanda su ka hau matakin albashi na GL13-GL15. Shugaban Malaman Makaranta reshen jahar Kano Comrade Baffa Ibrahim Garko ya ce, kungiyar Malaman Makaranta ba ta ji dadin rashin sa wa wasu malaman Primary Promotion da aka janye musu ba. A inda ya Kara da cewa , kungiyar ba ta San dalilin abun da jawo Hakan ba. Amma idan Allah ya Kai mu ranar Talata 2/1/2023 za su bi kadin wannan al'amari domin shawo kan matsala. Sannan ya Kara da ba wa malamai hakuri akan wannan rashin sa musu kudadensu na promotion. Comrade Auwalu Shuaibu Jae Dauke da rahoto@teachersmedia.com
NUT KANO STATE WING A yau Litinin 13/5/2024 Maigirma State NUT Chairman *Comrade Baffa Ibrahim Garko* ya kai ziyarar nuna jaje makarantar *GJSS Ɗanmali* akan mummunan harin da wasu iyayen yara su ka kai wa Vice principal ta makarantar a satin da ya gabata . Maigirma Chairman ya ƙara jaddada wa al'umma jahar Kano musamman iyayen yara da sauran mutanen gari ce wa, daga yanzu ƙungiyar malaman makaranta ta NUT ba za ta sake zuba ido ba wani ko wasu mutane su ke shiga har makaranta su na cin zarafin malaman makaranta ba. Ya kuma ƙara da ce wa, duk wanda aka sake samu da aika irin wannan munanan halaye na cin zarafin malaman makaranta, to sai inda ƙarfinsa ya ƙare. Comrade Baffa ya ƙara da ce wa, lallai malaman makaranta su tsaya su kare aikinsu yadda ya kamata. Kuma ƙun ƙungiyar NUT kofarta abuɗe ta ke wajan ganin an share wa kowanne malami hawayenshi a duk inda ya ke a duk faɗin jahar Kano. A inda shi kuma shugaban makarantar GJSS Ɗanmali ya ce , tabbas shi a yanzu ma ya fara s
Comments
Post a Comment